Tonon Asiri Bayan Rashin Lafiyar Maryam Yahaya Yanzu Wani Sabon Al’amari Ya Bulla

Idan Baku Mantaba Fitacciyar Jarumar Film Din Hausa Wanda Akafi Sani Da Maryam Yahaya Tayi Rashin Lafiyar A Kwanakin Baya Wanda Ake Tunanin Anyi Mata Asiri.
To A Yau Kuma Sai Muka Tashi Da Wani Sabon Al’amari Akan Rashin Lafiyartata, A Jiya ne Muka ga Jarumar Ta Wallafa Wasu Hotunan Guda Biyu A Shafinta Na Instagram Tare da Yin Bayani na Nuna Godiyarta Ga Allah Daya Bata Sauki.
Sai Dai Bayan Wallafa Wannam Hoto Nata Mutane Da Dama Sukayi Ta Daukan Hoton Suna Wallafawa A Shafukansu Na Sada Zumunta Facebook, Whatsapp Da Instgram.
Amma Abunda Yafi Jan Hankalinmu Anan Shine yadda Muka Ga Wasu Suna Yin Kurman Baki Akan Wanann Hoto Nata Ko Kuma Muce Tashinta Daga Rashin Lafiya..
Kamar Yadda Muka ga Mai Shafin Mufeeda Rasheed Ta Wallafa Hoton Jarumar Kamar Haka;
Acikim Bayanin Mufeeda Rasheed Take cewa Ki Godewa Allah, Sannan Wannan Ya Zamto Miki Darasi.
Wannan Bayani An Mufeeda Rasheed Shi Hausawa Suke Kira Da Barin Zance, Domin Kuwa Tayi Wasu Kalamai Wanda Ya Zamto Maganace Mai Harshen Damo.
Ma’ana Mai Dauke Da Wasu Sakonni Biyu Zamu So Mu Karbi Ra’ayoyinku Akan Wannan Batu Na Mufeeda Rasheed Ga Maryam Yahaya Wajen Tashinta Daga Rashin Lafiya Sannan Kuma Da Wadannam Kalamai Nata Mungode.
Munaso Ku Danna Alamar Kararrawa Domin Samun Sabbabin Shirye-shiryenmu Akoda Yaushe.