An Hallaka ‘yan bindiga aƙalla 32 a jihar Neja, waɗanda suka tsero daga Jihar Zamfara Wanda bayan aukuwar wannan lamarin ‘yan bindigar sun
An Hallaka 'yan bindiga aƙalla 32 a jihar Neja, waɗanda suka tsero daga Jihar Zamfara Wanda bayan aukuwar wannan lamarin 'yan bindigar sun

‘yan Bindiga sunkaiwa jami’an ‘yansandar wani mugun Hari Wanda suka illata da Dama sannan suka kashe mutum biyar.
A Yammacin yaune mukasamu saban rahotan daga Daya daga Cikin manema labaranmu na Dalatopnews Dake Jihar neja yatabbatar Mana da aukuwar lamarin.
Rahotan nacewa Jami’an tsaron haɗin guiwa sun hallaka yan bindiga aƙalla 32 a jihar Neja, waɗanda suka tsero daga Zamfara, kamar yadda PRNigeria ta rahoto.
Wannan ya biyo bayan harin da yan bindigan suka kaiwa jami’an tsaro, inda suka harbe yan sanda 5 har Lahira, waɗanda suka yi kokarin maida martani. Gumurzun ya faru ne a ƙauyen Bangu Gari, dake ƙaramar hukumar Rafi ta jihar Neja ranar Lahadi.
Wata majiya daga cikin jami’an tsaro ya bayyana cewa wasu yan bindiga da suka fito daga Zamfara saboda ruwan wutan sojoji, sun fara kafa sansani a yankin.
Majiyar tace: “Adadi mai yawa na yan bindigan ɗauke da muggan makamai, ciki harda roket, sun tattaru a yankin bayan tserowa daga sansaninsu dake Danjibga da Munhaye a ƙaramar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.
Ku cigaba da bibiyarmu a shafinnamu Domin samin Jin labaran Duniya a harkulum Kuna tare Dani A.Usman Ahmad a shafinmu na Dalatopnews.
KU KARANTA WANNAN:
Kyawawan Hotunan Da Najlat Muhd Tayi Na Bayan Aurenta Da Dan Kwallon Nijeriya Shehu Musa
Hazikar Sojan Ruwan Da Tayi Zarra Cikin Daliban NDA Da Aka Yaye A Wannan Shekarar
Daga yanzu babu wata adawa a tsakanina da gwamnatin jihar Kamo, cewar Mustapha Nabraska
Sabida Matsalar Tsaro A Kasa Nigeria A Kalla Mutane 41Suka Rasa ransu A Makon da yagabata.
Kada kumanta kudanna Mana alamar kararrawar sanarwa Domin samin Jin kararrawar shirye-shiryanmu masu kayatarwa mungode.