Yadda Al’ummar Unguwar Dakata Suka Kuka Kan Bude Gidan Sharholiya Da Ake Kukarin Yi A Unguwar
Yadda Al'ummar Unguwar Dakata Suka Kuka Kan Bude Gidan Sharholiya Da Ake Kukarin Yi A Unguwar

Wani Al’amari Da Ya Tada Hankula Mutanem Unguwar Dakata Dake Jihar Kano Shine Ta Yadda Ake Shirin Bude Gidan Sharholiya Dakan Iya Jawo Yawaitar Zina A Unguwar
Saide Kuma Kungiyar Arewa Tayi Ga Gwamnatin Jihar Kamar Haka ‘Kungiyar Marunutan Arewa A Kafafen Sadarwa Zamani ‘Arewa Media Writers’ Karkashin Jagorancin Shugaban Kungiyar Na Kasa Comr Abba Sani Pantami ,Da Shugaban Kungiyar Reshen Jihar Kano Comr Kabir Dakata Tana Kira Ga Gwamnatin Jihar Kano Da Sauran Masu Ruwa Da Tsaki Da Su Duba Kan Yunkurin Cutarwa Da Ake Kokarin Aikatawa Ga Al’ummar Unguwar Dakata Dake Kwayar Jihar Kano
Mu Sami Wannan Labari ne Daga Al’ummar Wannan Yanki Cewa ‘Rana Tsaka Aka Wayi Gari Anzo An Gina Wannan Katafaren Wajen Cikin Sirri Duk Da Kokarin Da Suke Wajen Tsaftace Unguwar Daga Munanan Dabi’u Musamman Shaye Shaye Da Harkokin ‘Sharholiya’ Ga Matasa
A Binciken Da Kungiyar ‘Arewa Media Write’ Ta Gabatar Ta Samu Labarin Cewa Mamallakin Wajen Ya Yaudari Wadanda Ya Sayi Wajen A Hannunsu Ne Da Kuma Dagacin Unguwar Dakata Alh Salisu Ibrahim Zubairu Kan Cewa Gidan Abinchi Zai Bude A Wannan Wajen Hakane Ya Bashi Dama Dinga Aikin Cikin Sirri Ba’ayi Aune Ba Rana Tsaka Sai Gani Akayi An Yi Fenti Kamar Yadda Za’a Gani Cikin Wayannan Hotuna
Bayan Kammala Bincike Na Tsanani Da Kungiyar Na Game Da Wannan Lamarin A Karshe Tana Mika Kokenta A Madadin Al’ummar Unguwar Dakata Zuwa Ga Gwamati Jihar Gwamna Da Duk Masu Ruwa Da Tsaki
Daga Karshe Suna Mai Neman Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje Zai Sharewa Mutane Unguwar Daka Hawayensu
Ku Kara Karanta Wannan Labarin
Zamu So Karben Ra’ayoyinku Game Da Wannan Lamarin.