Yanzu-Yanzu: Rikici ya barke a tsakanin jaruman shirin Izzar so Fatima Hamza P.A da Aisha Najamu da Nana
Yanzu-Yanzu: Rikici ya barke a tsakanin jaruman shirin Izzar so Fatima Hamza P.A da Aisha Najamu da Nana

Kamar yadda kuka sani ba sabon abu bane rikici ya kaure a tsakanin jaruman masan’antar kannywood wanda suke fitowa soshiyal midiya suna fadin maganganu kala-kala wanda daga baya kuma sai su sasanta tsakanin su.
Kamar yadda kowa ya sani Aisha Najamu da P A da kuma Minal Ahmad wanda aka fi sani da nana , dukkan su jarumai ne a cikin shirin Izzar so mai dogon zango.
A yanzu nan ne muka sani wani labari daga kafar sada zumunta na Instagram wanda jaruma Fatima Hamza wanda aka fi sani da P A ta cikin shirin nan mai dogon zango wato Izzar so, inda ta bayyana a cikin wata bidiyo tana fadin tarihin rayuwarta sannan kuma take fadin abubuwa wanda suka shafeta wanda ya kamata mutane su sani.
A cikin bayanin da tayi a bidiyon tana fadin cewa, akwai wata a cikin shirin Izzar so wanda take bayyana cewa Izzar so ya mata komai, amma tana ja musu aji wanda kuma ta dalilin shirin na Izzar so ta zama wata har ma duniya ta santa amma yanzu tana nuna halin ko inkula ga abokan aikin nata na shirin Izzar so da kuma wadanda suke shirye-shirye tare.
Domin kuji cikekken bayanin da jarumar tayi sai ku kalli bidiyon dake kasa domin kuji yadda ake rikicin da ita, da kuma yadda abin ya samo asali.
Ga bidiyon nan domin ku kalla.
Karanta wannan labarin.
Yanzu Hamisu Breaker Ya Bayyana Wanda Ya Kashe Auren Momi Gombe Sannan Ta Shigo Kannywood
Karanta wannan labarin.
An Kusan Kasheni Lokacin Danaje Saudiyya Dawafi Cewar Baba Ari Jarumin Kannywood
Karanta wannan labarin.
Wata mata ta bayyana yadda ake yaudaran su ake kaisu kasar Saudiyya da sunan aiki ana Lalata dasu