Rashin kuɗin a bincine da ba a bawa ƴansandaba shiyajanyo suka tada hargitsi a wajan bada sakamakon zaɓan.
Rashin kuɗin a bincine da ba a bawa ƴansandaba shiyajanyo suka tada hargitsi a wajan bada sakamakon zaɓan.

Yan sanda sun tayar da har gitsi a cibiyar tattara sakamakon zaben gwamnan Jihar Anambra saboda rashin biyan su kudadensu na aikin zaben.
Kamar yadda mukasani muna tsaka da labaran jihar anambra wanda rahoto ke nuna cewa sakamakon zaɓan na shirin kammalawa saidai wata daban daga gefe guda da muka samu cewa.
Fusatattun ƴan sandan sun dauki matakin da gula lissafin tattara sakamkon zaben ne a ofishin Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da ke Karamar Hukumar Anaocha ta Jihar Anambra a ranar Asabar da dare.
Wani mai sa ido kan yadda zaben ke gudana ya ce ana tsaka da aiki ne fusatattun ’yan sandan da aka kai daga Jihar Ondo suka kashe injin janareton da ke samar da wuta a cibiyar tattara sakamakon zaben.
A cewarsa, hakan na iya kawo babbar matsala ga zaben, amma daga baya an samu an shawo kan ’yan sandan, har aka sake kunna janareton aka ci gaba da aiki da shi.
Tun da farko mun kawo muku rahoton yadda wasu ƴan sandan da aka tura domin samar da tsaro a zaben suke kokawa cewa an ki ba su N5,000 da aka ware wa kowannensu a matsayin kudin abinci a lokacin zaben.
Wasu daga cikin ƴan sandan sun bayyana wa wakilinmu na Dalatopnews cewa yunwa ta yi musu kullin alawa, saboda rashin tanadar musu da kudaden abincinsu.
To jama’a zamuso mukarɓi ra ayoyin Ku akan aukuwar wannan lamari na jihar anambra domin jin tabakinku ku zaku iya biyomu kaitsaye ta sahinmu na tsokaci.
KU KARANTA WANNAN:
Kada kumanta ku danna mana alamar kararrawar sanarwa domin samun jin kararrawar shirye-shiryenmu Masu kayatarwa mungode.