Bayan harin da ƴan ta’adda suka kaiwa jirgin ƙasar dake sufuri zuwa Abuja Kaduna mutane sunƙi sakin jiki da jirgin dangujewa masu garkuwa da mutane.
Bayan harin da ƴan ta'adda suka kaiwa jirgin ƙasar dake sufuri zuwa Abuja Kaduna mutane sunƙi sakin jiki da jirgin dangujewa masu garkuwa da mutane.

Jirgin ƙasar dake sufuri zuwa Abuja Kaduna na bukatar tsaro na musamman.
Jirgin kasa da ke zama takamar ƴan bokon arewacin tarrayar Najeriyar ya fuskanci jerin hari har guda biyu a tsakanin 20 ga wata zuwa 21 ga watan Oktoban 2021.
Lamarin da ya tada hankali masu mulki da talakawan yankin da ke masa kallo a matsayin damar kauce wa barayin dajin da suke musu ɗauki dai dai.
Sai dai rundunar sojan kasar ta ce ta fara wani shirin tura jiragen sama da nufin shawagi kan layin dogon hanyar jirgin kasar da ke da tsawon kilomita kusan 200 da kuma ke zaman irinsa na farko na zamani da Najeriya ta kaddamar.
Duk da cewar ba bayani dalla-dalla na yawan jirage da lokacin shawagin dai, ana kallon matakin a matsayin kokari na karfafa gwiwar matafiya da dama suka koma kan tituna bayan harin da ya tada hankalin.
Matafiya da dama ciki har da Isma’il Yufu sun kaurace wa layin dogon bayan harin da ya kai ga jefa bam a kan layin ko bayan harbin matukin jirgin.
To jama’a zamuso mukarɓi ra ayoyin Ku akan wannan lamari don jin tabakinku zaku iya biyomu kaitsaye tasahinmu na tsokaci kaitsaye.
KU KARANTA WANNAN:
Tirkashi: An bayyana wani sabon al’amri akan jarumi Adam a zango akan auri sakin da yake
Mayaƙan ISWAP da suka kashe Janar Dzarma Zirkusu Sunga ta kansu a wajan sojojin Nigeria.
Yanzu Wani Bidiyon Maryam Yahaya Ya Ɓulla Na Sharholiya A Tiktok Masha Allah
Kada kumanta kudanna mana alamar kararrawar sanarwa domin samun jin kararrawar sanarwar shirye-shiryenmu Masu ƙayatar mungode.