A ranar Litinin mutum 12 aka kashe a Illela yayin da kuma ragowar ukun suka rasa rayukansu a Goronyo a jihar Sokoto.

A ranar Litinin mutum 12 aka kashe a Illela yayin da kuma ragowar ukun suka rasa rayukansu a Goronyo a jihar Sokoto.

Kimanin mutum 15 ne ake fargabar sun mutu a wani hari na ranar Lahadi da ƴan bindiga suka kai Kananan Hukumomi Goronyo da Illela na Jihar Sakkwato.

Gwamnan Jihar Aminu Waziri Tambuwal wanda ya tabbatar da hakan a ranar Litinin ya ce mutum 12 aka kashe a Illela yayin da kuma ragowar ukun suka rasa rayukansu a Goronyo.

Gwamna Tambuwal ya bayyana mana  haka ne jim kaɗan gabanin gabatar da Kasafin Kudin Jihar Sakkwato na shekarar 2022 a gaban Majalisar Dokokin jihar.

Tambuwal hare-haren sun auku ne a tsakanin daren Lahadi zuwa wayewar gari na Litinin a Kananan Hukumomin da lamarin ya shafa.

Gwamnan ya kuma mika ta’aziyyarsa ga ƴan uwan wadanda suka mutu da kuma wadanda suka jikkata a hare-haren da ƴan bindiga suka kai.

Bayanai sun ce Kananan Hukumomin biyu da lamarin ya shafa na daga cikin wadanda gwamnati ta bayar da umarnin katse musu layukan sadarwa a yunkurinta na kawo karshen matsalar tsaro a Jihar.

Duk wannan dai na faruwa ne a yayin da wasu rahotanni ke cewa ƴan bindiga sun fara daula a kauyuka da dama na Jihar Sakkwato inda har sun shata wa mazauna haraji da zasu dinga biya duk bayan wani lokaci.

KU KARANTA WANNAN:

 

Tofa In Baba Dan Audu Ne Babanka Wane Mataki Zaka Dauka Akansa ?, A Matsayinka Na Mai Hankali

Tofah Saurayin Daya Tonawa Nuhu Abdullahi Asiri Tare Da Ƙaryata Abunda Ya Faɗa Yanzu Ya Sake Wallafa Wani Batun Game Dashi

 

Bidiyan Gwamna Bala Muhamned Tare Da Yarsa Suna Rawa A Bikin Ta

 

Wani al’amari ya bayyana akan wasu jaruman kannywood wanda suka sauya kamanni bayan wasu shekaru

Kada kumanta kudanna mana alamar kararrawar sanarwa domin samun jin kararrawar sanarwar shirye-shiryenmu Masu ƙayatar mungode.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button