Mu cikakkun zaurawa ne muna bukatar maza su aure mu ni da kawayena, cewar jaruma Rashida Abdullahi mai sa’a
Mu cikakkun zaurawa ne muna bukatar maza su aure mu ni da kawayena, cewar jaruma Rashida Abdullahi mai sa'a

Tsohuwar jarumar masana’antar kannywood Rashida Adamu Abdullahi wacce aka fi sani da Rashida mai sa’a, ta bayyanawa duniya tana bukatar neman aure ga duk namijin daya shirya auren su yazo sun shirya.
Rashida mai sa’a ta sake jaddada wannan maganar da tayi bayan wanda tayi a shafinta na sada zumunta, alokacin da suke tattauna da wakilin jaridar Damukaradiyya inda take bayyana cewa.
Jama’a sun sani ni Rashida Abdullahi mai sa’a da kawaye na su Hadiza Kabara da Teema Yola da Jamila Nagudu, duk cikakkun zaurawa ne idan akwai wanda take son daya daga cikin mu to ya fito mun shirya.
Kuna zan tsaya masa a matsayin shugaban su don haka idan har da mai da mai bukatar auren mu to ya fito mun shirya.
Ganin cewar ana yiwa maganar da tayi kallon kamar da wasa take yi don haka ba lallai a sami wanda zai tsaya din ba, amma sai ta kara da cewa.
Babu maganar wasa indai mutum ya shirya din ya same ni duk wanda yake so a cikin mu idan an daidai ta abin bazai zo da wahala ba.
Don haka maza kada su dauka da wasa mu ke yi, mun shirya auren ga duk wanda ya shirya zai auren mu in dai da gaske ya ke yi.
Karanta wannan labarin.
Karanta wannan labarin.
Jami’ar ilorin ta kori ɗaliban makarantar ta da ya zane malamar su akan taƙi temakamar
Karanta wannan labarin.
Yadda Nafisat Abdullahi Ta Bayyana Dalilin Rigimarta Da Hadiza Gabon – Wata Sabuwa A Kannywood