Shugaban ƙasa ya ba wa sojoji umarni su tura karin makamai zuwa Sakkwato.
Shugaban ƙasa ya ba wa sojoji umarni su tura karin makamai zuwa Sakkwato.

Yan bindiga sun kashe akalla mutum 10 a Karamar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato, sa’o’i kadan bayan Shugaba Muhammadu Buhari ya umarci sojoji su yi amfani da karin makamai wurin murkushe bata-garin.
To jama’a kamar yadda muka kawo muku rahotan jiya wanda matasa sukayi tururuwa zuwa wajen mai girma shugaban kasar Nigeria ta zanga zangar lumana baiyan mai girma shugaban ƙasar Nigeria yayi magana ga abin da ya biyo baya wanda shine a binda matasan suke gudu.
Wani mazaunin garin Sabon Birni ya shaida wa Dalatopnews cewa maharan sun yi aika-aikan ne a wasu kauyuka da ke yankin Unguwar Lalle.
Ya ce ƴan bindigar sun kashe wani mai suna Abdullahi Usman a garin Unguwar Lalle, mutum tara a Tsangerawa da wasu mutum hudu a akauyen Tamindawa.
Sun kuma bude wa wani babur mai kafa uku wuta a kauyen Gajid inda suka kashe mutum uku nan take mutum biyar da suka samu raunin harbin bindiga kuma ana jinyar su a asibiti.
Maharan sun kuma yi garkuwa da mutum uku a wani kauye amma sun sako mutanen bayan kwana biyar da aka biya kudin fansa Naira miliyan biyu.
Amma Kwamishinan ƴan Sandan Jihar Sakkwato Kamaluddeen Okunlola ya ce mutum takwas ne aka kashe yana mai alkawarin daukar mataki a kan maharan.
Sun kai harin ne a wasu kauyukan da ke wajen gari da ba za a iya zuwa cikin sauki ba saboda rashin hanyoyi masu kyau.
Ko jiya da dare Shugaban Kasaa ya ba wa sojoji umarni su tura karin makamai zuwa Sakkwato inji Kwamishinan ƴan Sandan.
Wanda wannanne abinda matasan yankin ke gudu a ko da yaushe.
To jama’a zamuso mukarɓi ra ayoyin Ku akan aukuwar wannan lamari na Sokoto don jin tabakinku zamuso kubiyomu kaitsaye tasahinmu na tsokaci kaitsaye.
KU KARANTA WANNAN:
Tonon Asiri Yanzu Wata Budurwa Ta Bayyana Abunda Wasu ‘Yam Matan TikTok Sukeyiwa Samari
Yadda matata ta daure ni a jikin gado tamin shegen duka sannan ta gudu gidan su sabida ta fini karfi
Tirƙashi a daran jiya Laraba motar barasa ta faɗi a gaban ofishin shizba a jihar kano.
Kada kumanta ku danna mana alamar kararrawar sanarwa domin samun jin kararrawar sanarwar shirye-shiryenmu Masu ƙayatar mungode.