Advertisement

Daga Yanzu Bazan Sake Yin Garkuwa Da Mutane Ba Yanzu Na Saki Wayanda Suke Hanunmu Cewa Turji

Daga Yanzu Bazan Sake Yin Garkuwa Da Mutane Ba Yanzu Na Saki Wayanda Suke Hanunmu Cewa Turji

Rahotannin Daga Jihar Zamfara A Nijeriya Na Cewa Kasurgumin Dan Fanshi Dajin Nan Da Aka Fi Sani Da Suna Bello Turji Ya Saki Wasu Gomman Mutane Da Suka Dade Suna Tsare A Hannunsa

Rikakken Dan Fashin, Na Cikin Manyan Jagororin Yan Fashin Dajin Da Suka Fi Kaurin Suna Wajen Kashe -Kashe Da Satar Mutane Don Neman Kudin Fansa Musamman A Tsakanin Jihohin Zamfara Da Sokoto

Jaridar Daily Trust Ta Ambato Wasu Majiyoyi Da Ke Cewa A Watan Jiya, Bello Turji Ya Rubutawa Masarautar Shinkafi Wasika Inda Yake Jadadda Aniyyarsa Ta Hawa Teburin Tattaunawa Da Nufin Ajiye Makamansa Da Kuma Rungumar Zaman Lafiya

A Cewarta Sakin Gomman Mutanen Wani Bangare Ne Na Tattaunawar Da Ake Yi Da Turji

Bakin Gulbi Bello Turji Ya Ajiye Su A Kusa Da Kauyen Mabera

Da Misalin Karfe Biyar Na Maraice Zuwa Shida Shi Turji Ya Sako Wadannan Mutane Kuma Aka Je Aka Zo Dasu Zuwa Area Command Na Rundunar Yan Sanda Da Ke Nan Cikin Garin Shinkafi

Yace Ba Da Jimawa Ba Kuma Aka Wuce Da Su Zuwa Gusau Babban Birnin Jihar Zamfara

Ya Kara Da Cewa Wasu Cikin Yan Uwan Wadanda Aka Sakon Sun Gana Da Su Har Ana Murna

Da Aka Tambayi Wannan Shaidan Ko Me Kwaso Wadanda Aka Sakin Sai Ya Ce An Kawo Su Ne A Motoci , Bakin Gulbi Tutji Ya Ajiye Su A Kusa Da Kauyen mabera Da Yake Kusa Da Shinkafi

Inda Aka Bayyana Cewa Turji Ya Saki Dukka Wayanda Yayi Garkuwa Da Su Saboda San Ayi Sasantu Kamar Yadda Zakuga Bidiyan A Kasa

 

Masu Sauraranmi A Koda Yaushe Bayan Kun Kalli Wannan Bidiyan Zamu So Karben Ra’ayoyinku A Sahen Mu Na Tsokaci Sannan Muna Da Bukatar Inda Wannan Ne Karan Ka Na Farko Da Ka Dannan Mana Alamar Kararrawar Sanarwa Domin Samun Shirya Shiryanmu A Koda Yaushe.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button