Advertisement

HUKUNCIN TSOTSAR FARJIN MACE KO AZZAKARIN NAMJI HARAMUNNE NE??

HUKUNCIN TSOTSAR FARJIN MACE KO AZZAKARIN NAMJI HARAMUNNE NE??

HUKUNCIN TSOTSAR FARJIN MACE KO AZZAKARIN NAMJI HARAMUNNE NE??

Tambaya

:

Shin ko ya halatta ga miji ya tsotsi gaban matarsa ko ita mace ta tsotsi gaban mijinta ko ko kuma ta sha maniyyinsa??

:

​​Amsa:​​

:

​Asali dai a ​shari’ance​ ya halatta mace da miji suyi abin da a ke ƙira da suna ​(Al-Istimtā’u)​ wato ​jin daɗī tsakanin ma’aurata,​ danhaka ya halatta suji daɗi da junansu yadda sukaga dama, sai dai abin da ​shari’a ta keɓance tayi hani a kansa,​ kamar a ce ​miji​ ya sadu da ​matarsa​ a lokacin da ta ke cikin ​jinin al-ada ko jini bīƙi,​ ko kuma ​miji​ ya sadu da ​matarsa​ ta ​duburar ta​ ko rgaduwa da ita lokacin da ta ke yin ​azumin farilla.

:

Danhaka kenan idan ​miji ya tsotsi farjin matarsa​ ko ita ​mace ta tsotsi azzakarin mijinta​ Malamai sukace duk ya halatta, saboda hakan zai iya shiga ne cikin ​Ƙarƙashin​ hukuncin ​(Al-Istimta’u)​ wato jindaɗī tsakanin ​ma’aurata. Saboda ​faɗin Aʟʟãн(ﷻ)​ cewa:​

:

​”نساؤكم حرث لكم فأتوا حرثكم أني شئتم” (البقرة/الآية223)​

​​MA’ANA:​​

​​Matanku Gonakan ku ne, danhaka ku zowa gonakan ku ta inda duk kuka ga dama:​​

:

​A cikin wata ​ayar​ kuma ​Aʟʟaн(ﷻ)​ Ya ce:​

:

​”هن لباس لكم وأنتم لباس لهن”​

​​MA’ANA:​​

​​(Mātanku) tufāfi ne a gareku, haka kūma (Mazajensu) tufafi ne a garesu.

:

​Amma idan ya kasance a na da tabbas ko zato mafi rinjaye gameda cewa yin hakan zai iya haifarwa wani daga cikinsu wata cūta ko kuma ya kasance babu wata cūta da hakan zai haifar sai dai kawai ​ɗaya daga cikin ma’auratan​ baya son a yi masa hakan to ​Malamai​ sukace bai halatta suyi hakan ba dan gudun kada a cūtar da wanda ba ya so ɗin, sai dai wasu daga cikin ​Malamai​ suna ganin duk da cewa yin hakan ba haramun ba ne to amma barinsa shi yafi alkhairi:

:

​Amma dangane da ​magana​ akan hukuncin cewa idan ​mace tana tsotsar azzakarin mijinta​ har ya kai ga yin ​Inzali (fitar maniyyi)​ a cikin bakinta, shin ya halatta ta haɗiye wannan ruwan ​maniyyin​ ko bai halattaba? ​Alal-Haƙiƙa a nan Malamai sunyi saɓãni​ a kan wannan ​Mas’ala,​ kuma ​saɓãnin​ na su ya ginu ne a kan mas’alar cewa shin maniyyi najasa ne​ ko ba najasa ba ne? ​Malaman​ da suka tafi a kan fahimtar cewa ​maniyyi najasa ne​ sukace haramun ne mace ta sha, domin ba ya halatta ga ​Mutum Musulmi​ ya ci ko ya sha dukkan abinda ya kasance najasa ne.

:

​Sai dai ​Magana​ mafi Inganci kamar yadda wasu daga cikin ​Malamai suka rinjayar itace,​ cewa ​maniyyi​ ba najasa ba ne, to amma sai dai ​Malamai​ sukace duk da kasancewar maniyyi abu ne ​mai tsarki ba najasa ba,​ sukace bai kamata a ce ​Mutum​ ya sha ​maniyyiba. domin yin hakan yana daga cikin ​ƙazanta,​ kamar yadda bai kamata ba a ga ​Mutum​ yana shan ​Majina, duk da cewa ​majina​ ba najasa ba ce amma ko shakka babu cewa shanta ɗin ​ƙazanta ne.

:

※(шαʟʟαнυ-тα’αʟα α’αʟαмυ)※

:

▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂

Daga Zaυren

Fιƙ-нυl-Iвadaт

▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂▂

Mυѕтαρнα Uѕмαи

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button