Cin Amana Wannan Cin Amana Dame Yayi Kama, Wannan Mutumen Bashida Imani, Ɗan Maƙwabcin Sa
Cin Amana Wannan Cin Amana Dame Yayi Kama, Wannan Mutumen Bashida Imani, Ɗan Maƙwabcin Sa

Cin Amana: Wannan Cin Amana Dame Yayi Kama, Wannan Mutumen Bashida Imani, Ɗan Maƙwabcin Sa.
MATSALAR TSARO
Dangi kuzo gareni a yau zani baku zance
Akan batun tsaron nan da ya barmu yau a zauce
Yau ba tsumi garemu, dabara ko sai a zance
Domin jinin mutanenmu ake ta kyalayarwa
Ɓarnar tana yawa; mu faɗi babu kauce-kauce
Ana ta haihuwar guzuma, ɗa, uwa a kwance
Kullum muna tunanin ya ranmu zai kasance
Idan sukai nufin su kashe babu mai hanawa
Birni da ƙauyuka, hantsi har zuwa maraice
Idan suna kisa har mara lafiya na kwance
Sun ƙona dukiyoyi, sun barmu mun talauce
Har soja ma gudunsu suke babu me tsayawa
Waɗansu sun tare hanya sunyi kwance-kwance
Satar mutum suke a biya, anƙi rai su fauce
Dangi su saida duk kadarorinsu har da rance
Su fanshi ɗan’uwansu a hannunsu ba tsayawa
Dukkan ta’annatin da suke nabi na karance
Batun ana tayin galaba kansu duk bula ce
Duk mai faɗin akwai nasara barshi zai kurumce
Ƙarya fure take bata ɗiya irin na maiwa.
Idan kana waya kayi katari da masu kwace
Ka basu ko su far maka sara su barka kwance
Polis batun tracking a wajensu ja’iba ce
Sai dai ka barwa Allah shi ne yake mayarwa
A Borno ko masifar sai dai kawai kwatance
Har sansanin gudun hijarar tasu ya ƙazance
Fyaɗe da karuwanci da bara da cuce-cuce
Sauƙi ko sai wajen Allah Rabbi mai iyawa
Wani ɗan’uwa yace Nasiru ai kawai ka mance
Wahala tasa na ƙyale ‘yata a karuwance
Sai tabi ‘yan maza sun ɗauketa sun kaɗaice
Sannan mu samu lomar ci ko abin ciyarwa
Ya sake ce dani matata fa ta makance
‘Ya’ya maza guda uku ta huɗunsu ‘yar macen ce
Biyu sun ɓatan dabo an nemesu babu dace
Sai addu’a nake gun Allahu ba gazawa
Kaiconmu ‘yan’uwa wai ko shirunmu fa’ida ce?
Muna gani ana sara mutum kamar itace
Daba a lungunanmu da gayunga masu ƙwace
Tsoro ya samu ko tari babu me iyawa
Batun tsaron ƙasar nan wallahi yaudara ce
Na kasa gane shin wai koma manaƙisa ce?
Ina janar janar ɗin ko duk uwar ɗarin ce?
Sai mai tarewa oga hanya kuke kashewa?
Kai ɗan’uwa tsaya kaji karma ka sakankance
Ba mu a zuciyar mai mulkinmu karka mance
Ka nemi kariyar Allah safe har maraice
Shi ne kawai yake hana azzalumai sakewa
Ko ni da nai rubutun nan zuci na amince
Ba dan tsaron Ilahu ba da na daɗe a kwance
Ina su Dadiyata yau babu sai a zance
Sai ko da mun tuno su hawayenmu suyi zubowa
Kana gani fa har ‘ya’yayenmu an farauce
An kaisu can kudanci an sasu yin barance
An canja harsuna; addininsu anyi ƙwace
Batun a ɗau mataki kuwa babu mai kulawa
Wani shugaba cikinmu da yaji zuciyarsa kwance
Yace da duniya ai sakaci muke a sace-
‘Ya’yanmu, da da iko ɗauremu zai a mance
Ai dolema a rainamu a dinka hallakarwa
Zan cigaba, insha Allahu
©Nasir Ahmad Sadiq