KINA FAMA DA YAWAN MANTUWA, TO GWADA YIN WANNAN

KINA FAMA DA YAWAN MANTUWA, TO GWADA YIN WANNAN
MAGANCE YAWAN MANTUWA.
– Za a samo kirfat sai arika tafasa cokali daya anasha koko arika tafasa rabin cokali dasafe asha, haka dayamma idan aka dage kan wannan za a rabu da wannan matsala.
– Ko kuma a samo kamun sai a tafasa cokali daya a hada da maul khal cokali daya asha amma kamun din kullum kofi daya za a sha insha Allah zaasami biyan bukata.
Ko a rika hada Na’a Na’a a na tafasawa da zuma a na sha.
– Ko a samo luban zakar a rika tafasawa a na sha insha Allah za a rabu da yawan mantuwa.
Amma idan ana zargin matsalar tana da alaqa da jinnu domin zasu iya haifar ma mutum da wannan matsala suma…….
To sai a samo ruwan zamzam a karanta wadannan ayoyi fatiha,
Ayatul kursiyyu,
Amanarasulu,
Suratul Kafirun
Suratul Ikhlas
Falaki,
da Nasi,
Sai arika shan ruwan zamzam din ana shafawa ajiki.
Idan kuma ana iyawa sai ahada da dubbu samawi, da kuma dubbu adri, wato shi Alkur’ani, da kuma magungunan Muslinci wadanda nakawo.
Allah yasa mudace ameen.